World News

Tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya ce, magajin kujerarsa Shugaba Bola Tinubu, yana taka rawar gani sosai tun bayan hawansa mulki…

Tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya ce, magajin kujerarsa Shugaba Bola Tinubu, yana taka rawar gani sosai tun bayan hawansa mulki.

Watanni tara da suka gabata zuwa yanzu

Tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya ce, magajin kujerarsa Shugaba Bola Tinubu, yana taka rawar gani sosai tun bayan hawansa mulki watanni tara da suka gabata zuwa yanzu.

Tsohon shugaban kasar ya ce, Tinubu ya taka rawar gani idan aka yi la’akari da yanayin da ake ciki, sai dai ya tabbatar da cewa Nijeriya wata kasa ce mai sarkakiya wajen gudanar da mulki.

Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugaban hukumar kwastam, Bashir Adewale Adeniyi da jami’an gudanarwar hukumar a garin Daura na jihar Katsina a karshen mako da muka yi bankwana da shi.

Tinubu ya fuskanci suka sosai kan wasu manufofinsa na tattalin arziki da suka hada da cire tallafin man fetur da lamuran da suka shafi hada-hadar canjin kudi.

Wadannan tsare-tsare da wasun su sun haifar da hauhawar farashin kayayyaki da tabarbarewar tattalin arziki da faduwar darajar Naira, wanda a ‘yan kwanakin nan ya haifar da zanga-zanga a fadin kasar.

Leadership Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button